in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar ANC ta zargi masu yunkurin hallaka shugaban kasar Venezuela
2018-08-06 11:27:45 cri
Jam'iyyar ANC mai mulkin Afrika ta kudu ta zargi masu rajin nuna fin karfi dake kokarin kifar da gwamnatin kasar Venezuela da yunkurinsu na hallaka shugaba Nicolas Maduro.

A wata zantawar da ta yi da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ANC ta ce, a bayyane take karara cewa dakaru masu rajin sauya shugabancin kasar ba su amince ko kuma girmama 'yancin kasar da al'ummar kasar ta Venezuela ba, da kuma gwamnatin da aka zaba ta hanyar demokaradiyya.

Shugaba Maduro ya tsallake rijiya da baya daga wani yunkurin harin da aka kai masa ta jirgin sama marar matuki a ranar Asabar. A kalla wasu ababen fashewa biyu ne aka gano sun fado a gaban shugaban kasar daga cikin jirgin, a daidai lokacin da Mista Maduro ke gabatar da jawabin cika shekaru 81 da kafuwar rundunar tsaron kasar.

Maduro ya dora alhakin harin kan wasu dake yakar gwamnatinsa a cikin kasar ta Venezuela da kuma wata makarkashiya daga gwamnatin Amurka.

ANC ta yi Allah wadai da kakkausar murya da harin, ta kara da cewa, wannan kazamin aiki abu ne da ba za'a taba amincewa da shi ba a tsarin demokuradiyya da kuma masu son zaman lafiyar duniya.

Jamiyyar ANC ta bukaci gwamnatin Venezuela da ta binciko masababbabin harin kana ta yi dukkan kokarinta wajen kama wadanda ke da hannu kan lamarin.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China