in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya taya al'ummar Najeriya murnar cika shekaru 58 da samun 'yancin kai
2018-10-01 20:19:33 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya rubutawa takwaransa na Najeriya Muhammadu Buhari wasikar muranr cika shekaru 58 da samun 'yancin kai, yana mai bayyana cewa, a karkashin jagorancinsa al'ummar kasar ta himmatu wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki da inganta rayuwar jama'a da ma samun sakamako mai gamsarwa.

Shugaba Xi ya ce ya yaba da gudummawar da shugaba Buhari ya bayar wadda ta kai ga samun nasarar taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da aka cimma a birnin Beijing na kasar Sin, da darajanta ci gaban alakar kasashen biyu. Yana kuma fatan hada kai da shugaba Buhari wajen daga matsayin alakar kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare zuwa wani sabon matsayi ta yadda za ta yi amfana al'ummomin kasashen biyu.

Bugu da kari, shugaba Xi ya yi fatan samun kyakkyawar makoma da farin ciki ga Najeriya gami da al'ummominta. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China