in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasar Sin sun kai gaisuwar ban girma ga mazan jiyan kasar a filin Tian'anmen
2018-09-30 16:18:42 cri
Shugabannin Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, sun kai gaisuwar ban girma ga mazan jiyan kasar a wajen tunawa da su dake filin Tian'anmen.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, kuma Janar Sakatare na JKS, kana shugaban rundunar sojin kasar, na cikin dimbin jami'an da suka fito don tunawa da mazan jiyan, a jajibirin ranar murnar kafuwar sabuwar kasar Sin.

Sauran manyan jami'an da suka hallara sun hada da Li Keqiang da Li Zhanshu da Wang Yang da Wang Huning da Zhao Leji da Han Zheng da Wang Qishan. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China