in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin addini a Kamaru sun yi tir da rikicin dake wakana a yankunan kasar dake amfani da Turancin Ingilishi
2018-09-20 09:45:02 cri
Shugabannin majalisun addinin kirista da Islama a Kamaru, sun yi tir da rikicin dake wakana a yankuna 2 na kasar masu amfani da Turancin Ingilishi na kudu maso yamma da arewa maso yammacin kasar.

Sanarwar da shugabannin addinan suka fitar, ta yi tir da kisan kiyashin da sojoji da mayakan Amba Boys ke wa 'yan kamaru.

"Amba Boys" shi ne sunan da 'yan Kamaru ke kira 'yan awaren dake yunkurin neman kafa sabuwar kasa mai suna "Ambazonia".

Sanawar ta kuma ruwaito shugabannin addinan na yin tir da hare-haren da ake kai wa cibiyoyin ilimi da take hakkin yara na samun ilimi, suna masu sukar matakai marasa karfi da suka ce gwamnati ta dauka na shawo kan matsalar.

Shugabannin wadanda suka ce suna magana ne da murya daya kuma da yawun dukkan mabiya addinai, sun jadadda cewa, hawa teburin sulhu ne hanyar warware rikicin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China