A yau Litinin aka bude taron wayar da kan jama'a, game da kimiyya da fasaha na duniya a nan birnin Beijing hedkwatar kasar Sin, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da sakon taya murnar bude taron.
Cikin sakonsa, shugaban ya ce ta hanyar sanya kasashe daban daban bude kofarsu, da kuma yin hadin gwiwa tsakaninsu, za a iya tabbatar da ganin ci gaban kimiyya da fasaha, ya kara taka muhimmiyar rawa ga ci gaban al'ummar bil Adama. (Bello Wang)