in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya taya murnar gudanar da bikin ranar kiyaye zaman lafiya ta duniya ta shekarar 2018
2018-09-19 13:35:21 cri
A yau ne aka gudanar da bikin ranar kiyaye zaman lafiya ta duniya ta shekarar 2018 a birnin Nanjing dake lardin Jiangsu na kasar Sin.

A sakonsa na taya murna shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi nuni da cewa, zamantakewar al'umma tana begen samun zaman lafiya. Kasar Sin ta tsaya tsayin daka kan manufar samun bunkasuwa cikin lumana, da kokarin shimfida zaman lafiya da samun bunkasuwa da ganin an martaba dokokin kasa da kasa a duniya.

Xi Jinping ya jaddada cewa, taken ranar a wannan shekara shi ne "kokarin kafa al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil'adama da yin kokari tare wajen gina duniya mai cike da zaman lafiya da tsaro", wanda ya dace da tunanin da ya kai ga kafa ranar kiyaye zaman lafiya ta duniya da ma muradun kasashen duniya da al'ummominsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China