in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matsananciyar matsin lamba daga Amurka ba za ta durkusar da tattalin arzikin kasar Sin ba
2018-09-28 09:31:41 cri
Ma'aikatar kula da harkokin cinikayya ta kasar Sin, ta ce matsananciyar matsin lamba daga Amurka ba za ta durkusar da tattalin arziki ko tsoratar da kasar ba.

Yayin wani taron manema labarai da ya kira a jiya, kakakin ma'aikatar Gao Feng, ya ce kasar Sin za ta yi amfani da kalubalen wajen kara ingantawa da bunkasa tsarin tattalin arzikinta, tare da samar da ci gaba mai inganci.

Ya ce kasar Sin ta kasa tantance ainihin dalilan da suka sanya Amurka bullo da sabbin halayya, kuma Sin din ba ta goyon bayan sanya siyasa cikin harkokin tattalin arziki da cinikayya ba. Ya ce kofar kasar a bude take don tattauna yadda za a warware batun da Amurka, amma dole ne tattaunawar ta kasance bisa gaskiya da adalci da cika alkawurrra.

Ya ce yuwuwar tattaunawar da kuma lokacin da za a yi, za su dogara ne kan Amurka.

Gao Feng ya ce ya kamata Amurka ta fahimci yanayin sosai, sannan kada ta raina batun warware rikicin da yakini da kuma karfin kasar Sin.

Har ila yau, ya ce suna fatan za a warware takaddamar cinikayya da tattalin arziki dake tsakanin kasashen biyu, amma kuma sun shiryawa duk wani abu da- ka-je-ya-zo. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China