in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta kusa yin bankwana da ambaliyar ruwa da ya addabi sassan kasar
2018-09-27 09:36:33 cri
Gwamnatin Najeriya ta sanar a jiya Laraba cewa, alamu sun nuna cewa ambaliyar ruwan da ta yi mummunar barna a sassan kasar ta yammacin Afrika ta kusa zuwa karshe.

Da yake jawabi ga manema labarai bayan kammala taron majalisar zartaswa ta kasa a Abuja babban birnin kasar, ministan albarkatun ruwa na kasar Suleiman Adamu, ya ce alamu sun nuna cewa ibtila'in ambaliyar ruwan ya zo karshe wanda ya shafi a kalla jahohin kasar 10.

Adamu ya ce, ruwan da ya tumbatsa daga madatsar ruwa ta Lagdo daga jamhuriyar Kamaru wanda ke makwabtaka da Najeriyar ya fara komawa daidai tun a ranar Asabar din da ta gabata, kuma wannan wata alama ce dake nuna cewa ruwan dake ambaliyar ya fara janyewa.

Ya ce adadin ruwan a Lokoja, wanda daya ne daga cikin biranen da ambaliyar ta yi mummunar barna, ya ragu da kusa sentimita 6 kuma yana ci gaba da raguwa.

A bisa ga kididdigar da hukumar bada agajin gaggawa ta kasar (NEMA) ta fitar, kimanin mutane 441,251 ne ambaliyar ruwan ta shafa daga kananan hukumomi 50 dake sassan Najeriyar.

A wani rahoton da aka fitar game da halin da ake ciki a ranar Litinin, hukumar bada agajin gaggawa ta kasar ta ce mutane 108 ne suka mutu sanadiyyar ambaliyar ruwan kana wasu 192 kuma sun samu raunuka. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China