in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Cutar amai da gudawa ta hallaka mutane 61 a jihar Yobe dake arewacin Najeriya
2018-09-21 19:29:41 cri
Mahukuntan jihar Yobe dake arewa maso gabashin Najeriya, sun tabbatar da rasuwar mutane 61, baya ga wasu 50 dake kwance a asibiti, sakamakon kamuwa da cutar amai da gudawa ko cholera.

Wasu alkaluma da gwamnatin jihar ta fitar, sun nuna cewa, yawan wadanda suka kamu da cutar sun kai mutane 906, cikin watanni 2 da suka gabata.

A Juma'ar nan ne dai fadar gwamnatin ta Yobe, ta ayyana barkewar cholera a jihar, tana mai cewa cutar ta yadu cikin kananan hukumomin jihar 6.

Cutar amai da gudawa dai na yaduwa ne ta hanyar amfani da ruwa maras tsafta. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China