in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Antonio Guterres ya yi kira da aka kara kwazo wajen amfani da matakan siyasa a ayyukan wanzar da zaman lafiya
2018-09-26 10:21:06 cri
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi kira da a kara azama, wajen amfani da matakan siyasa, a ayyukan wanzar da zaman lafiya. Yana mai cewa ana aikewa ne da jami'an wanzar da zaman lafiya, domin su share fage ga abun da zai biyo bayan tafiyar su, don haka kulla kyakkyawar alaka da al'ummun da suke wa aiki ke da matukar fa'ida.

Mr. Guterres na wannan tsokaci ne, a jawabin da ya gabatar, albarkacin taron wanzar da zaman lafiya da aka yiwa lakabi da A4P, a wani bangare na taron kolin MDD karo na 73 dake gudana yanzu haka a helkwatar MDDr dake birnin New York.

Ya ce "kare fararen hula aiki ne mai matukar muhimmanci da ya rataya a wuyan jami'an wanzar da zaman lafiya. Kuma ba za mu taba mantawa da mummunan sakamakon dake biyo bayan gazawar mu ba".

Daga nan sai ya jaddada kira ga sassan masu ruwa da tsaki na yankuna da kasashe, da su ci gaba da fadada hadin gwiwa da juna, matakin da a cewar sa, zai taimaka matuka ga cimma nasarar matakan siyasa, da na gudanarwa, masu nasaba da ayyukan wanzar da zaman lafiya.

Mr. Guterres ya kuma jinjinawa jami'an wanzar da zaman lafiya masu aiki a nahiyar Afirka, yana mai cewa "Idan akwai bukatar yaki da ta'addanci, ko wanzar da zaman lafiya, dakarun dake aiki a nahiyar, ciki hadda wadanda kungiyar AU ke turawa, na taka rawar gani yadda ya kamata. Don haka ya yi kira ga kasashe mambonin MDD, da su marawa irin wadannan ayyuka baya, ta hanyar samar da kudade isassu kuma a kan lokaci.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China