in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe mambobin MDD sun sha alwashin koyi da manufofin siyasar Mandela
2018-09-25 10:54:33 cri
Wakilan kasashe mambobin MDD dake halartar taron koli karo na 73 na majalissar, sun sha alwashin bin tafarkin siyasa na tsohon shugaban kasar Afirka ta kudu Nelson Mandela, wanda ya kunshi yunkurin samar da duniya mai cike da adalci da martaba rayuwar bil Adama.

Wakilan wadanda suka kunshi shugabannin kasashe da manyan kusoshin gwamnatoci, sun bayyana hakan ne jiya Litinin, yayin taron tattauna batutuwa da suka shafi zaman lafiya, wanda aka sadaukar ga Nelson Mandela, sun kuma amince da wani kuduri na farko yayin taron na bana, mai take "Zage damtse ga martaba juna, da juriya, tare da fahimtar juna, da cimma maslaha tsakanin sassa daban daban."

Har ila yau, wakilan kasashen sun jaddada muhimmancin cimma nasarar ajandar wanzar da ci gaba ta nan da shekarar 2030, suna masu cewa za su tsaya tsayin daka wajen cimma nasarar sassan ta 3, da suka hada da raya tattalin arziki, da kyautata zamantakewa da kare muhalli, a yanayin daidaito da hade dukkanin sassa.

A tsokacinsa game da batun, babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya ce rayuwar Mandela ta alamta dukkanin kudurorin MDD, duba da yadda ya sadaukar da rayuwar sa ga hidimta wa al'umma.

Mandela ya kasance lauya, wanda ya yi zaman gidan yari, kana ya zamo mai shiga tsakani, mai kuma wanzar da zaman lafiya. Kana tsohon shugaban kasa wanda daga karshe ya zamo dattijo da ake martabawa.

A watan Disambar shekarar 2017, mambobin MDD suka yanke shawarar gudanar da taro na farko na MDD game da zaman lafiya, a matsayin bikin cikar Mandela shekaru 100 da haihuwa. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China