in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya jadadda bukatar inganta shugabanci na gari da tabbatar da adalci yayin da ake aikin wanzar da zaman lafiya
2018-09-22 15:54:53 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya amince da wani kuduri a jiya, wanda ke da nufin inganta ayyukan jami'an wanzar da zaman lafaiya a dukkan matakai, tare da jadadda bukatar inganta shugabanci na gari da tabbatar da adalci.

Kwamitin wanda daukacin mambobinsa suka amince da kudurin mai lamba 2436, ya yi kira ga Sakatare Janar na MDD da ya tabbatar da shirye-shiryen wanzar da zaman lafiya na majalisar na da adalan shugabannin wadanda suka dace.

Sannan ya bukace shi, da ya sanya bayyanan ayyukan wanzar da zaman lafiya, wanda ya takaita matakan da aka dauka na inganta ayyukan shirye-shiryen da shawo kan kalubaken dake tattare da su, cikin rahoton da zai mikawa kwamitin.

Kwamitin ya bayyana damuwa game da zargin cin zarafi ta hanyar lalata da ake wa jami'an wanzar da zaman lafiya, tare da tabbatar da goyon bayansa ga manufar sakatare Janar na majalisar, ta rashin lamuntar kowanne irin nau'i na cin zarafi ta hanyar lalata.

Kwamitin ya kuma bukaci dukkan kasashe dake bada gudunmuwar 'yan sanda da dakaru da su tabbatar da jami'an sun kai mizanin MDD a fannin kwarewa da horo da kayayyakin aiki da kuma tabbatar da aiwatar da aikin da aka dora musu bisa nuna kwarewa da dabi'u na kwarai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China