in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasashe gami da kusoshin gwamnatoci 128 za su halarci taron kolin MDD
2018-09-21 14:00:16 cri
Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya bayyanawa kafofin watsa labarai a jiya Alhamis, a hedikwatar majalisar dake birnin New York cewa, akwai shugabannin kasashe 84, gami da kusoshin gwamnatoci 44, wadanda za su halarci taron kolin MDD a makon gobe, inda za a yi babbar muhawara, ta babban taron MDD karo na 73.

Guterres ya ce, halartar wadannan shugabanni gami da kusoshin gwamnatocin kasashe daban-daban, na shaida irin amincewar da kasashen duniya suke nunawa MDD. Guterres ya ce, zai yi amfani da wannan dama, don neman kasashe daban-daban, su yi sabon alkawari ga MDD, kasancewar ta dandalin tattauna hadin-gwiwar kasa da kasa da ba za'a iya rayuwa ba bu ita ba. Har wa yau, Guterres ya nuna damuwa, game da "yadda wasu bangarori daban-daban ke nuna kyama" ga ra'ayin halartar kasashe daban-daban a harkokin duniya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China