in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci kungiyoyin gama kai na Afirka da su inganta ajandar kare muhallin nahiyar
2018-09-16 15:45:53 cri
Hukumar kare muhalli ta MDD ta yi kira ga kungiyoyin gama kai na kasashen Afirka(CSOs) da su taimaka wajen tsara muhimmiyar ajandar kula da muhalli da za ta taimaka wajen aiwatar da manufofi da ayyukan da suka dace a bangaren kare muhalli da samun ci gaban mai dorewa.

Darekta kana wakiliyar ofishin hukumar mai kula da nahiyar Afirka, Juliette Biao Koundenoukpo ita ce ta bayyana hakan yayin bude taron dandalin manyan kungiyoyi da masu ruwa da tsaki na Afirka na kwanaki biyu da ya gudana a birnin Nairobin kasar Kenya. Tana mai cewa kasashen nahiyar za su iya amfani da hanyoyi da matakan su na diflomasiya wajen canja ajandar nahiyar game da muhalli.

Ta ce kungiyoyin gama kai za su taimaka wajen inganta matakan kirkire-kirkire na kasashen nahiyar game da tunkarar kalubalen muhalli da nahiyar take fuskanta.

Jami'ar ta ce, akwai bukatar kasashen na hanzarta canjawa daga tsarin da aka saba gudanarwa a baya zuwa hanyoyi da matakan da suka dace domin magance batutuwa kamar karuwar tsadar kudaden makamashi da batun talauci da lalacewar muhalli, da gurbatar iska da rashin daidaiton tsakanin jama'a.

Ta ce, kasashen nahiyar na da karfi da ilimin kirkiro matakan magance kalubalen muhalli da suke fuskanta. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China