Jami'an tsaro sun shaidawa kamfanin dallancin labarai na kasar wato MENA cewa, al'amarin ya auku ne a yankin Heliopolis na Cairo.
Sanarwar da ministan sufurin jiragen sama na kasar, Mohamed Younis al-Masri ya fitar, ta ce wasu tankoki biyu mallakar wani kamfanin mai ne suka fashe a kusa da filin jirgin saman birnin Cairo.
Ya ce dukkan jirage na ciki da wajen kasar na zirga-zirga kamar yadda suka saba.
Ya kara da cewa, fashewar ta auku ne saboda zafi da ya yi yawa, kuma an yi nasarar takaita gobarar. (Fa'iza Mustapha)