in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Amurka zai ziyarci Koriya ta Kudu da Sin da Japan game da batun kawar da makaman nukiliyar Koriya ta arewa
2018-09-07 14:48:37 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Amurka, ta ce wakilin kasar na musamman mai kula da batun Koriya ta arewa, Stephen Biegun, zai kai ziyara manyan biranen Koriya ta Kudu da Sin da Japan, daga ranar 10 zuwa 15 ga wannan wata, domin tattauna batun kawar da makaman nukiliyar Koriya ta Arewa.

Sanarwar da ma'aikatar ta fitar a jiya, ta ce Stephen Biegun zai gana da takwarorinsa tare da ci gaban hadin gwiwar diflomasiyya domin cimma nasarar kawar da makaman baki daya, kamar yadda Shugaba Kim ya amince da shi a Singapore.

Shugaba Kim ya shaidawa wakilin Koriya ta Kudu a ranar Laraba cewa, zai goyi baya tare da tabbatar da ganin an kawar da duk wani hadarin yaki daga zirin Koriya, tare da mayar da shi dandalin zaman lafiya da babu makamai ko barazanar nukiliya.

Da yake mayar da martani a jiya Alhamis, Shugaban Amurka Donald Trump, ya wallafa a shafinsa na Tweeter cewa, yana godiya ga shugaba Kim bisa furucin da ya yi, inda ya ce za su tabbatar da aikin kawar da makaman nukiliya daga zirin Koriya a tare. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China