Sanarwar da ma'aikatar ta fitar, ta ce mutanen da aka sanyawa takunkumin 'yan kasar Syria ne da Lebanon, sauran kuma kamfanoni ne dake Syria da Lebanon da Hadaddiyar Daular Larabawa.
Ta kara da cewa, takunkuman na nuni da cewa, Amurka za ta ci gaba da daukar kwararan matakan tilasta yanke duk wani taimako ga gwamnatin Assad da maso goya mata baya. Haka kuma, za ta ci gaba da amfani da duk wani mataki dake akwai, na mayar da gwamnatin Assad saniyar ware. (Fa'iza Mustapha)