in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a samar da agaji ga mutanen da rikici ya shafa a Somalia
2018-09-04 10:57:22 cri
Wakilin MDD a Somalia Justin Brady, ya yi kira ga al'ummomin kasa da kasa da su bada taimako mai dorewa ga mutanen da rikici da farin bara da ambaliyar ruwa a bana ya shafa a Somalia.

Justin Brady, wanda jami'i ne a ofishin kula da harkokin jin kai na MDD, ya yi gargadin cewa, duk da yanayin samun abinci ya ingantu a kasar, har yanzu akwai wasu mutane masu yawa dake fuskantar rashin abincin.

Sanarwar da jami'in ya fitar a jiya, ta ce bukatun agajin gaggawa da al'ummomi daban-daban ke fuskanta akai-akai, ya sa sun kasa farfadowa. Sannan samun kudin agajin jin kai da zai shafe shekaru da dama abu ne mai matukar wahala.

A cewar UN, duk da ana samun ruwa da ya zarce matsakaicin mataki a lokutan damuna 2 da ake da su, akwai mutane miliyan 4.6 ciki har da yara miliyan 2.5 dake bukatar agajin jin kai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China