Rundunar sojin Amurka ta ce harin da dakarunta na musammam suka kai ta sama, ya hallaka mayakan al-Shabaab 27 a arewacin Somaliya.
Rundunar sojin Amurka dake aiki a Afrika (AFRICOM) ta ce an kai harin na ranar Asabar ne da hadin gwiwar gwamnatin Somaliya, a kudu maso yammacin birnin Bosaso.
Wata sanarwar da AFRICOM din ta fitar, ta ce, babu fararen hula da harin ya rutsa da su.
Harin, shi ne na baya-bayan nan cikin jerin hare-haren da dakarun Amurka ke kaiwa kasar dake yankin kahon Afrika da hadin gwiwar dakarun Tarayyar Afrika.
Ana kai galibin hare-haren ne kan jagororin al-Shabaab da sansanoninsu dake kudancin Somaliya, inda har yanzu kungiyar ke rike da wasu yankuna. (Fa'iza Mustapha)