in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron kolin Tehran:Kasashen Iran, Rasha da Turkiya za su tattauna batun Syria
2018-09-04 10:31:15 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran Bahram Qasemi ya bayyana wa taron manema labarai na mako-mako cewa, kasashen Rasha da Turkiya da Iran mai masaukin bakin taron kolin kasashen uku da zai gudana a birnin Tehran, za su mayar da hankali wajen tattauna tashin hankalin dake faruwa a kasar Syria da ma matakan samar da zaman lafiya a kasar dake yankin kasashen Larabawa.

Ya ce, batun yaki da ayyukan ta'addanci na kan gaba cikin ajandar ganawar, sauran sun hada da batutuwan kasa da kasa da na shiyya-shiyya da kuma batutuwa da ke shafarsu.

Kasashen uku dai su ne ke kokarin ganin an cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Syria, kuma tun a shekarar 2016 suke kokarin shiga tsakani a shirin tabbatar da zaman lafiya game da rikicin kasar ta Syria.

A ranar Jumma'a mai zuwa ne ake sa ran shugaba Hassan Rouhani na Iran da takwarorinsa na kasashen Rasha Vladimir Putin da na Turkiya Recep Tayyip Erdogan za su gana a birnin Tehran na kasar Iran. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China