in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya sake goyon bayan yarjejeniyar nukuliyar Iran bayan da Trump ya sake dawo da takunkuman da aka dagewa kasar
2018-08-08 10:28:24 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya sake jaddada muhimmancin yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran da aka cimma a shekarar 2015, a matsayin daya daga cikin manyan nasarorin harkokin diflomasiya da aka cimma a 'yan shekarun nan.

Guterres wanda ya bayyana hakan ta bakin kakakinsa Farhan Haq, ya kuma yi imanin cewa, yarjejeniyar ta cancanci a ci gaba da goyon bayanta, kuma akwai bukatar sassan da yarjejeniyar ta shafa su martaba kunshin dake cikinta.

Jami'in na MDD na wadannan kamalai ne, bayan da shugaba Donald Trump na Amurka ya janye kasarsa daga yarjejeniyar kana jiya Talata ya sake dawo da takunkuman da aka janyewa kasar ta Iran.

Ya ce, ko yaya kasa, gwamnati ta dauki wannan batu, MDD ba ta magana a kan manufofin cikin gidan kowa ce kasa.

A jiya ne dai umarnin da shugaba Trump ya bayar na sake kakabawa kasar ta Iran takunkumi,da kuma dakatar da yarjejeniyar nukiliyar kasar(JCPOA) ya fara aiki, bayan da tun farko ya fice daga yarjejeniyar Iran din da aka cimma da kasashen Turai. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China