in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran:Burtaniya ta maye gurbin Amurka a fannin sake fasalta na'urar tace ruwa ta Arak
2018-08-23 10:28:52 cri
Shugaban hukumar kula da makamashi ta kasar Iran Ali Akbar Salehi, ya bayyana cewa, Burtaniya ta maye gurbin kasar Amurka a cikin kungiyar dake kula da sake fasalin na'urar dake tace ruwa ta Arak dake tsakiyar kasar ta Iran.

Jami'in wanda ya sanar da hakan ta kafar talabijin din kasar, ya ce an dauki wannan mataki ne, sakamakon ficewar da kasar Amurka ta yi daga yarjejeniyar nukiliyar kasar da kasashen duniya suka cimma (JCPOA).

A halin da ake ciki kuma, Salehi ya ce, janyewar Amurka daga yarjejeniyar ba ta shafi ayyukan Iran na samun makamashin nukiliya cikin lumana ba, ciki har da hakowa, da yin bincike da rayawa ko gina sabbin tashohin samar da makamashi da wasu ayyukan, kamar samar da magunguna ko gina asibitoci.

Ya ce, ayyukan makamashin nukiliyar kasar na gudana babu wata matsala. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China