Shugaba Xi ya bayyana hakan ne a yau Litinin yayin da yake yiwa taron shugabanni da wakilan 'yan kasuwan Sin da Afirka jawabi.
Ya ce, a shirye kasar Sin take ta karfafa alakarta da kasashen Afirka ta yadda za a gina hanyar ci gaba mai inganci da ta dace da yanayin kasashen, ta yadda kowa ne bangare zai ci moriya.
Jawabin shugaban mai take "aiki tare don samun kyakkyawar makoma" shi ne kuma taron 'yan kasuwar Sin da Afirka karo na shida. (Ibrahim)