in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta taimakawa kasashen Afirka wajen horas da kwararru fiye da dubu 200 cikin shekaru 3 da suka gabata
2018-09-03 09:39:47 cri
A wani taron kara wa juna sani game da taron kolin kungiyar hada kan kasar Sin da kasashen Afirka FOCAC da aka shirya a ranar 1 ga watan Satumba, wasu tsoffin direktoci 3 na sashen kula da harkokin Afirka na ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin,sun bayyana manufofin da kasar Sin ta dauka kan kasashen Afirka, da huldar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka da kuma yadda ake sharen fagen taron kolin na shekarar 2018. Sun bayyana cewa, a cikin shekaru 3 da suka gabata bayan shekarar 2015, gwamnatin kasar Sin ta samar da kudin tallafin karatu ga dalibai dubu 30 wadanda suka fito daga kasashen Afirka kuma suke karatu a nan kasar Sin, har ma ta taimakawa kasashen Afirka wajen horas da mutanen dake da fasahohin zamani iri- iri fiye da dubu 200.

Sannan kasar Sin tana kuma kokarin taimakawa kasashen Afirka a gwagwarmayar yaki da talauci, kuma sun riga sun fitar da wasu kwararan matakan yaki da talauci. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China