Li Keqiang ya gana da wasu shugabannin kasashen Afirka
A jiya Lahadi 2 ga watan Satumbar nan ne firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya gana da shugabannin kasashen Mauritius, da Kwadebuwa, da Masar, da Saliyo, da Afirka ta kudu da kuma Sudan, wadanda suka iso nan kasar Sin, domin halartar taron kolin dandalin hadin kan kasashen Sin da Afirka FOCAC. (Sanusi Chen)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku