Antonio Guterres ya bayyana UNRWA a matsayin muhimmiyar hukumar dake tallafawa 'yan gudun hirar Falasdinu tare da bada gudummuwa ga tabbatar da zaman lafiya a yankin, da samar da ingantaccen ilimi da kiwon lafiya da kuma biyan sauran muhimman bukatun 'yan gudun hijirar.
A don haka, ya yi kira ga sauran kasashe su taimaka su cike gibin kudi da hukumar ke fuskanta, domin ta ci gaba da gudanar da ayyuakanta. (Fa'iza Mustapha)