in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fasahohin Sin za su taimakawa Tanzania wajen raya tattalin arziki, in ji kakakin gwamnatin kasar
2018-09-01 17:04:46 cri
Kakakin gwamnatin kasar Tanzania Hassan Abbas, ya ce fasahohin kasar Sin sun zama abin koyi ga kasarsa, kuma shirin "Ziri daya da hanyar daya" zai taimakawa kasar wajen raya tattalin arzikinta.

Ya ce, bisa jagorancin Jam'iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kasar Sin ta cimma sakamako da dama wajen neman ci gaba, ta kuma tsara tsarin gurguzu na musamman da ya dace da yanayin da take ciki.

Ya kara da cewa, tarihin kasar Tanzania ya yi kama da na kasar Sin, sannan ita ma ta gamu da matsala wajen raya tattalin arzikinta, shi ya sa, fasahohin kasar Sin na raya tattalin arziki, za su iya zama abin koyi ga kasar.

Hassan Abbas Ya kuma kara da cewa, a yayin da kasar Sin take dukufa wajen neman ci gaba, tana kuma ba da taimako ga wasu kasashe domin neman ci gaba tare, yana mai cewa shirin "Ziri daya da hanya daya" da kasar Sin ta fitar a shekarar 2013, ya kuma ba da tallafi ga kasashen duniya da dama. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China