in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Ruwanda ya yabawa taron FOCAC
2018-09-01 17:02:51 cri
Daga ranar 3 zuwa ranar 4 ga watan Satumba, za a yi taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka. Taken taro na wannan karo shi ne "hadin gwiwa domin cimma moriyar juna, mu hada kanmu domin karfafa dunkulewar kasashen Sin da Afirka". A Kwanakin baya, shugaban kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU, kana shugaban kasar Ruwanda Paul Kagame, ya bayyana cewa, dandalin tattauna hadin gwiwar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka na da muhimmiyar ma'ana wajen habaka hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin biyu. Ya ce, taron ya kasance kyakkyawar dama ga mambobi kasashen wajen tattauna yadda za su habaka tare da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu.

Haka kuma, ya ce, shawarar "Ziri daya da hanya daya" na sa ran raya kasashen Asiya, Afirka har ma da kasashen Turai, domin cimma moriyar juna. A halin yanzu, kasar Sin ta himmantu wajen shiga cikin ayyukan gina ababen more rayuwa a kasashen Afirka, musamman ma kan ayyukan shimfida layin dogo da tashar samar da wutar lantarki da dai sauransu, lamarin da ya ce ya tallafawa al'ummomin kasar Ruwanda.

Kana, dangane da zargin da wasu mutane ke yi wa kasar Sin game da harkokinta a kasashen Afirka, Mr. Kagame ya ce, kasashen Afirka sun san abun da suke bukata, ta yadda za su iya samun ci gaba, da kuma yadda za su daidaita huldar dake tsakaninsu da manyan kasashen duniya. A ganinsa, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka na da muhimmiyar ma'ana ga bangarorin biyu wajen samun ci gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China