Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana a yau Asabar, da takwarorinsa na wasu kasashen Afrika, gabanin taron koli na dandalin tattaunawar Sin da Afrika na bana,wanda za a yi a nan birnin Beijing, a farkon mako mai kamawa.
Shugabannin kasashen Afrikan sun hada da Danny Faure na Seychelles da Patrice Talon na Benin da Peter Mutharika na Malawi da George Weah na Liberia da kuma na Guinea Alpha Conde. (Fa'iza Msutapha)