in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban majalissar dattawan Najeriya ya bayyana aniyar tsayawa takara a babban zaben kasar na badi
2018-08-31 09:16:11 cri
Shugaban majalissar dattawan Najeriya Bukola Saraki, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a babban zaben da zai gudana a farkon shekara mai zuwa.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne, Bukola Saraki, wanda mukaminsa ke a matsayi na 3 a jerin mukaman shugabancin Najeriyar, ya tabbatar da zai shiga a fafata da shi a neman wanda jam'iyyarsa ta PDP za ta tsayar takarar shugabancin Najeriya.

Da yake tsokaci game da hakan yayin wani taro da ya gudanar a Abuja fadar mulkin kasar, shugaban majalissar dattawan ya ce, yana da dukkanin abun da ake bukata na gogewa domin ciyar da Najeriya gaba.

A ranar 31 ga watan Yulin da ya gabata, Saraki ya sauya sheka daga jami'iyyar APC mai mulki zuwa tsohuwar jam'iyyarsa ta PDP, lamarin da ta haifar da cece kuce a tsakanin magoya baya na jam'iyyun biyu.

Bayan komawar tasa PDP ne kuma, jagororin jam'iyyar suka ayyana shi a matsayin uban jam'iyyar na kasa. Kafin nan, shugaban majalissar dattawan ya taba bayyana aniyarsa ta fafatawa da shugaban kasar mai ci wato Muhammadu Buhari, a zaben watan Fabarairun shekarar 2019 dake tafe. Sauran manyan 'yan siyasar dake neman shugabancin Najeriyar sun hada da tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China