Wani kwamandan hukumar kare aukuwar hadurra a titunan Najeriya Abdullahi Ibrahim ya bayyana cewa, mutanen sun gamu da ajalinsu ne nan take lokacin da motar bas din da suke ciki mai daukar fasinjoji 27 ta yi taho mu gama da wata motar dake zuwa. An kuma garzaya da mutane 16 da suka jikkata zuwa asibiti mafi kusa don a yi musu magani.
Jami'in ya ce hadarin ya faru ne sakamakon gudun da ya wuce kima da wuce motoci ba bisa ka'ida ba da direbobin ke yi a kan hanya. (Ibrahim)