in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Cutar Kwalara ta yi sanadin mutuwar mutane 28 a Nijeriya
2018-08-15 11:14:39 cri
Mutane a kalla 28 ne aka tabbatar da mutuwarsu sanadiyyar barkewar cutar kwalara a jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya, cikin watanni 7 da suka gabata.

Kwamishinan lafiya na jihar Kabiru Getso, ya shaidawa manema labarai cewa, an samu mutane 400 da suka yi fama da matsananciyar gudawa, inda aka tabbatar da 50 daga cikinsu sun kamu da cutar kwalara a fadin kananan hukumomi 33 na jihar.

Daga cikin mutane 50 da aka tabbatar da sun kamu, guda 28 sun mutu, yana mai cewa gwamnatin jihar ta dauki matakai da dama na takaita yaduwar cutar.

Ya ce matakan sun hada da ci gaba da sanya ido kan yankunan dake fuskantar barazanar barkewar cutar tare da binciko wadanda ke fama da amai da gudawa.

Kwalara matsananciyar cuta ce da alamominta ke farawa da gudawa, wanda kuma kan kai ga asarar rai idan ruwan jikin mutum ya kare.

Ana yawan samun barkewar cutar a Nijeriya saboda rashin kyawun hanyoyin samun tsaftataccen ruwa, musammam a yankunan dake da cunkoson jama'a. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China