in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta yi watsi da rahotannin dake cewa shugaban kasar na fuskantar matsi daga kasashen ketare don ya janye daga sake tsayawa takara
2018-08-15 11:20:05 cri
Fadar Shugaban Nijeriya ta yi watsi da rahotannin da wasu kafafen watsa labarai na kasar ke yadawa, wanda ke cewa shugaban kasar Muhammadu Buhari, na fuskantar matsin lamba don ya janye daga sake tsayawa takara.

Jaridar Daily Independent dake da mazauni a birnin Lagos na kasar, ta wallafa cikin kanun labaranta na jiya cewa, "Buhari na fuskantar matsin lamba don ya janye daga sake tsayawa takara"

Mashawarci shugaban kan kafafen watsa labarai Femi Adeshina, ya yi tir da labarin yana mai bayyana shi a matsayin na bogi.

A cewarsa, Shugaba Buhari ba mutum ne mara tunani ba, domin sai da yi nazari mai zurfi kafin ya bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara.

Ya kara da cewa, wadanda suke tsoron ba za su kai batansu ba idan ya tsaya takara ne ke kokarin sanyaya masa gwiwa ta kowace fuska, ciki har da labaran jaridu da aka dauki nauyinsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China