in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan kula da sufurin jiragen saman Najeriya na fatan taron kolin FOCAC zai samar da alfanu ga Sin da Najeriya
2018-08-28 12:23:03 cri

Karamin ministan kula da harkokin sufurin jiragen saman tarayyar Najeriya Hadi Sirika, ya ce, yana fatan taron koli na dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka wanda zai gudana a makon gobe a nan birnin Beijing, zai haifar da alfanu ga Najeriya da Sin, har ma da nahiyar Afirka baki daya, haka kuma yana maraba da Sin ta kara zuba jari a kasarsa da sauran wasu kasashen Afirka.

Yayin da yake zantawa da wakilin gidan rediyon CRI a baya-bayan nan, Hadi Sirika ya ce, Najeriya na maida hankali sosai kan taron kolin FOCAC a wannan karo, abun da a cewarsa, zai kawo karin damammaki wajen karfafa hadin-gwiwa tsakanin Sin da Najeriya. Ya ce, kamfanonin kasar Sin na ayyukan shimfida layukan dogo da gina filayen jiragen sama a Najeriya, har ma a kwanakin baya, Najeriya da Sin sun rattaba hannu kan wata sabuwar kwangilar gina hanyoyin mota. Sirika na fatan taron kolin na wannan karon, zai kara samar da moriya ga Najeriya da Sin har ma ga Afirka baki daya a fannoni da dama, ciki har da zaman rayuwar al'umma, da al'adu, da kuma siyasa.

Har wa yau, Hadi Sirika ya ce Afirka na da dimbin albarkatu, kana, Sin na da karfi sosai wajen raya tattalin arziki da kimiyya da fasaha, don haka yana fatan ganin kasar Sin ta kara zuba jari a kasarsa Najeriya da ma sauran wasu kasashen Afirka.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China