in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron Afrika da kasar Sin zai cimma nasara
2018-08-18 16:07:00 cri
Kwamishiniyar Tarayyar Afrika mai kula da harkokin al'umma, Amira Elfadil, ta bayyana fatan taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Kasar Sin da Afrika FOCAC, zai cimma nasara.

Amira Elfadil wadda ta bayyana haka a jiya, lokacin da take karban sabon Jakadan kasar Sin a Tarayyar Liu Yuxi, ta ce hukumar kula da ayyukan AU za ta taka muhimmiyar rawa ta hanyar shiga a dama da ita a taron da zai gudana da farkon watan Satumba a nan birnin Beijing.

A cewarta, FOCAC ya zama taron da ke gudana tsakanin Sin da Afirka akai akai, kuma akwai wani gagarumin aiki da hadin gwiwar bangarorin biyu zai samar karkashin taron na FOCAC.

Shugaban hukumar AU, Moussa Faki Mahamat tare da wasu manayn jami'an tarayyar ne za su halarci taron na Beijing, inda ake sa ran rattaba hannu kan yarjejeniyoyin fahimtar juna a bangarori mabambanta.

Da yake ganawa da Xinhua, Jakada Liu ya ce yayin taron, shugabannin Sin da Afrika za su tattauna kan bangarorin da za su hada gwiwa kansu a shekaru masu zuwa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China