in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in Habasha: ana zura idon ganin taron kolin Beijing na FOCAC zai inganta nasarorin da aka samu wajen hadin kan Sin da Afirka
2018-08-22 09:56:05 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Habasha Meles Alem ya bayyana a kwanan baya cewa, kasarsa na zura ido kan taron kolin dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da kasashen Afirka wato FOCAC da zai gudana a birnin Beijing, inda take fatan a yayin taron zai kara kyautata nasarorin da aka samu a fannin hadin kai tsakanin bangarorin biyu.

Meles Alem ya bayyana haka ne a yayin da yake zantawa da wakilinmu, ya kuma nuna yabo sosai kan tallafin da Sin ta dade tana baiwa kasashen Afirka, a cewarsa hadin kai a tsakanin Sin da kasashen Afirka hadin kai ne na na zaman daidai wa daida da samun moriyar juna, kasar Sin tana girmama 'yancin kasashen Afirka a fannin siyasa, kuma tana tallafawa kasashen Afirka ba tare da gindaya wasu sharuda ba.

Ban da wannan kuma, kasar Sin ita ce ta biyu a fannin tattalin arziki a duniya, hakan zai taimaka matuka ga ci gaban Afirka.

Baya ga haka, Meles Alem ya bayyana cewa, shawarar "Ziri daya da hanya daya" da Sin ta gabatar na da amfani wajen karfafa hadin kai a tsakanin Sin da kasashen Afirka. Ayyukan zuba jari da Sin ke yi kan manyan kayayyakin more rayuwar jama'a a kasashen Afirka na da ma'ana kwarai ga ci gabansu, kana kuma ba za a iya raba taimakon da kasar Sin ke baiwa kasashen Afirka ba wajen gudanar da ayyukan manyan kayayyakin more rayuwa. Ya zuwa yanzu, yawan jarin da Sin ta zuba a Habasha ya kai dala biliyan 4, Sin ta kuma nuna goyon baya ga Habasha a fannonin fasaha da kudi, don raya manyan kayayyakin more rayuwa da aikin samar da makamashi. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China