in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sudan ta kudu za ta sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta karshe
2018-08-23 10:25:32 cri
Bangarorin da ba sa ga maciji da juna a kasar Sudan ta kudu, sun amince su sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiyar kasar ta karshe a ranar Litinin mai zuwa idan Allah ya kai mu.

Ministan watsa labaran kasar kana kakakin gwamnati Micheal Makuei shi ne sanar da hakan ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua. Ya ce, bangarorin sun cimma daidaito kan galibin batutuwan da suke takaddama a kansu yayin zagaye na uku na tattaunawar zaman lafiyar kasar da aka fara ranar 13 ga watan Agusta a birnin Khartoum na kasar Sudan.

Ya ce, tattaunawar ta yanzu za ta mayar da hankali ne kan batutuwan da ba a warware ba, da yarjejeniyar raba madafun iko da ma matakan tsaro.

Sai dai kuma Makuei ya ce sun tattauna a kan batutuwan da suka shafi ikon mataimakan shugaban kasa, da kafa kwamitocin da za su tsara kundin tsarin mulki, da kwamitin shari'a da yawan jihohi da iyakokinsu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China