in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar sa ido game da rikicin Sudan ta kudu ta jinjinawa yarjejeniyar da aka cimma
2018-08-08 19:36:18 cri
Hukumar JMEC mai sa ido game da rikicin Sudan ta kudu, ta jinjinawa yarjejeniyar da aka cimma, tsakanin sassan da ba sa ga maciji da juna a kasar.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a birnin Juba, JMEC ta yi maraba da sanya hannu kan yarjejeniyar da tsagin gwamnati da na 'yan adawar Sudan ta kudun suka yi, a birnin Khartoum, fadar mulkin kasar Sudan, tana mai kira da a tabbatar an aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata.

Hukumar ta kuma yi maraba, da matsaya daya da aka cimma, game da wasu muhimman batutuwa da sassa masu adawa da juna a Sudan ta kudun ke takaddama a kan su. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China