in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jamus za ta ci gaba da yaki da bakin haure
2018-08-15 13:17:09 cri
Shugabar kasar Jamus Angela Merkel ta yi jawabi a jiya game da manufofin bakin haure na Turai da kasar Jamus ta gabatar, inda ta ce Jamus ta na hadin gwiwa da Faransa da Italiya da kungiyar EU wajen yaki da bakin haure da suke zuwa nahiyar Turai ba bisa doka ba daga kasar Nijer.

Merkel ta yi hira da 'yan kasar Jamus fiye da 50 game da makomar kasar, inda ta ce ana bukatar kungiyar EU ta raya dangantakar abota tsakaninta da kasashen Afirka don hana bakin hauren kasashen tafiya nahiyar Turai.

Merkel ta bayyana cewa, kasashen Afirka suna iya kwashe bakin hauren da suka shiga nahiyar Turai ba tare da samun izni ba, kana kasashen Turai sun shirya samar da damar karatu da aiki ga 'yan ciranin kasashen Afirka dake son zuwa Turai bisa doka.

Merkel ta kara da cewa, abu ne mai wuya a cimma yarjejeniyar bakin haure da kasashen Afirka, amma Turai tana bukatar irin wannan yarjejeniya. Ta ce ya kamata kasashen Turai su gudanar da wasu ayyuka don sa kaimi ga bunkasa nahiyar yadda ya kamata.

Merkel za ta gana da shugaban kasar Nijer Mahamadou Issoufou a ranar 15 ga wannan wata a kasar Jamus, inda za su tattauna batun bakin haure. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China