in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar Merkel ta samu raguwar magoya baya, yayin da Jam'iyyar AFD ta samu gagarumin ci gaba
2017-09-25 11:19:39 cri
Jam'iyyar masu ra'ayin rikau wato Conservative ta shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel, za ta ci gaba da yin rinjaye a majalisar dokokin kasar wato Bundestag, inda ta samu kashi 32.5 cikin dari na kuri'un da aka kada, adadin da ya yi kasa da kaso 9 idan aka kwatanta da zaben da aka yi shekaru 4 da suka gabata.

Ita ma babbar jam'iyyar adawa ta 'yan gurguzu wato SPD da tsohon shugaban majalisar dokokin Tarayyar Turai Martin Schulz ke jagoranta ta samu gagarumin koma baya.

Sai dai ba zato, jam'iyyar AFD ta samu gagarumin ci gaba inda ta samu kaso 13.5 na kuri'un, al'amarin da ya sanya ta zama jam'iyya mai karfi ta uku a majalisar dokokin kasar.

A wani jawabin da ta yi bayan zaben da aka watsa ta talabijin, Merkel ta shaidawa magoya bayanta cewa, manufofin gwamnatinsu a bayyane suke, kuma babu wata gwamnati da za a kafa ba tare da su ba, ta na mai tabbatar da cewa jam'iyyarta ta cimma nasara a zaben duk da cewa ta yi fatan samun sakamakon da ya fi wannan. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China