in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar gwamnatin Jamus ta yaba da gudummawar da kasar Sin ta bayar ga harkokin G20
2017-05-04 13:26:15 cri
Shugabar gwamnatin kasar Jamus, madam Angela Merkel ta bayyana a jiya Laraba cewa, a matsayin kasar dake jagorantar kasashe masu karfin tattalin arziki wato G20, Jamus na yin hadin-gwiwa mai kyau tare da kasar Sin, wadda ta jagoranci kungiyar G20 a karon da ya gabata.

Madam Angela Merkel ta yabawa kasar Sin saboda babbar gudummawar da ta bayar a fannonin da suka shafi tinkarar matsalar sauyin yanayi, da gudanar da cinikayya cikin 'yanci da sauransu, haka kuma ta ce, Jamus na fatan yin hadin-gwiwa tare da kasar Argentina wadda za ta jagoranci kungiyar G20 a karo mai zuwa, ta yadda harkokin kungiyar za su ci gaba da bunkasa.

Karfafa hadin-gwiwa tare da kasashen Afirka, wani batu ne da Jamus ke kokarin gudanarwa. A cewar Merkel, ya kamata kasashen G20 su yi koyi da kasar Sin a fannin raya hulda da Afirka. Merkel ta kuma ce, kasar Sin ta samu dimbin nasarori a fannonin kawar da kangin talauci, da habaka tattalin arziki, tare kuma da inganta muhimman ababen more rayuwar al'umma.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China