in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwmnatin Jamus ta tsaida kudurin kara jibge sojoji a kasashen Afghanistan da Mali
2018-03-09 11:08:03 cri
Gwamnatin kasar Jamus ta amince da shirin daidaita jibge sojoji a kasashen ketare da ma'aikatar tsaron kasar ta gabatar, inda ta tsaida kudurin kara jibge sojojinta a kasashen Afghanistan da Mali, tare kuma da habaka ayyukan soja a kasar Iraki.

Bisa wannan shirin, sakamakon tabarbarewar yanayin tsaro da kasashen biyu ke ciki, sojojin da Jamus za ta aike zuwa Afghanistan za su karu daga 980 zuwa 1300, kana wadanda za su shiga shirin kiyaye zaman lafiya na MDD a Mali su ma za su karu daga 1000 zuwa 1100. Baya ga haka, gwamnatin Jamus, ta tsaida kudurin aika sojoji zuwa Baghdad, babban birnin kasar Iraki. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China