Rahotanni daga kauyen da wannan lamari ya faru sun nuna cewa, mayakan sun aukawa kauyen ne da almurun jiya Litinin, inda bayan hallaka wasu mazauna wurin, suka kuma cinnawa wasu gidaje da dama wuta, lamarin da ya yi matukar tada hankulan mazauna kauyen, kamar dai yadda Baba Ali Daudu, wani mazaunin kauyen na Munduri ya bayyana. (Saminu Hassan)