Gidan talabijin na kasar na Nile, ya ruwaito cewa, yayin wani gagarumin biki da ya gudana a majalisar dokokin kasar, Shugaba Sisi ya yi rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasa. Inda ya rantse zai kare tsarin Jamhuriya na kasar da girmama kundin tsarin mulkin kasa da kare muradun jama'a da kiyaye 'yancin kan kasar da hadin kan yankunanta.
Jiragen yakin Masar da jirage maso saukar ungulu ne suka yi wa jerin gwanon motocin tsohon kwamnadan sojin rakiya zuwa hedkwatar majalisar dokokin kasar. (Fa'iza Mustapha)