in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD zai tsawaita aikin tawagar wanzar da zaman lafiya a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya
2018-08-11 16:12:20 cri
A jiya Juma'a kwamitin sulhun MDD ya sanar da cewa zai sake sabunta aikin tawagar dakarun wanzar da zaman lafiya na MDD a jamhuriyar Afrika ta tsakiya (UNOCA) zuwa wasu karin shekaru uku masu zuwa.

Kwamitin sulhun ya bayyana cewa tuni babban sakataren MDD Antonio Guterres ya amince da tsawaita aikin tawagar ta UNOCA zuwa karin shekaru uku nan gaba, wato daga ranar 1 ga watan Satumbar 2018 zuwa 31 ga watan Augastan shekarar 2021. Kwamitin sulhun ya bayyana aniyarsa na amincewa da wannan batu, kamar yadda sanarwar kwamitin sulhun MDDr ta bayyana.

Kwamitin sulhun MDDr ya bukaci Guterres da ya sake duba game da batun wa'adin aikin tawagar ta UNOCA ya kuma mika mata shawarwarin da ya zartar kafin ranar 1 ga watan Augastan shekarar 2019. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China