in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi kira da a kawar da makaman nukiliya a duniya
2018-08-09 10:58:47 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi kira da a kawar da daukacin makaman nukiliya dake doron duniyarmu. Guterres ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da wakilan mutanen da makamin nukiliya ya halaka a biranen Hiroshima da Nagasakin kasar Japan.

Ya ce, MDD za ta hada kai da wadanda makamin kare dangin ya yiwa illa domin ganin an kawar da makaman nukiliyar kwata-kwata a duniya.

A ranar Talata ne Guterres ya isa kasar Japan, a ziyarasa ta biyu zuwa kasar tun bayan da ya hau kan wannan mukami. Ya kuma gana da firaminista Shinzo Abe na Japan jiya da safe.

A ranar 6 da kuma 9 ga watan Agustan shekarar 1945 ne sojojin Amurka suka jefa makamin kare dangi a biranen Hiroshima da Nagasaki na kasar Japan, don tilastawa Japan ta yi saranda a yakin duniya na biyu. A ranar 15 ga watan Agustan shekarar 1945, kasar ta Japan ta mika wuya ga sojojin kawance, abin da ya kawo karshen yakin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China