in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi maraba da sakamakon taron kungiyoyin yankunan Afrika
2018-08-03 09:51:07 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi maraba da sakamakon taron da ya gudana tsakanin kungiyoyin kasashen yankunan tsakiya da yammacin Afrika.

Antonio Guterres, ya kuma yi maraba da sabon kudurin mambobin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS da takwararta ta kasashen yankin tsakiyar Afrika, na karfafa hadin kai a kan kalubaken tsaro da zaman lafiya.

Sanarwar da kakakinsa Farhan Haq ya fitar, ta ruwaito cewa, Guterres ya yi na'am, musammam da matakin da aka dauka ranar Litinin yayin taron da ya gudana a Lomen kasar Togo, na rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa kan yaki da manyan laifuffuka ya zuwa karshen 2018, da kuma kafa kwamitin ministoci da zai kula da aiwatar da matakan da aka dauka yayin taron. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China