in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: Shugaba Kabila ba zai tsaya takara ba
2018-08-09 16:21:50 cri
Babban magatakardan MDD Antonio Guterres ya yaba da matakin da shugaba Joseph Kabila na Jamhuriyar demokiradiyar Congo ya dauka na kin tsayawa takara a babban zaben kasar da za a yi.

Mataimakin kakakin Guterres Farhan Haq ya shaidawa taron manema labarai cewa, MDD ta ji sanarwar da gwamnatin Congon ta bayar cewa, Emmanuel Ramazani Shadary ne zai yiwa jami'iyyar dake mulki takara a zaben shugabancin kasar.

Ya ce, MDD ta kuma yi maraba da ci gaban da aka samu, wanda zai kai ga gudanar da zaben gaskiya da adalci a ranar 23 ga watan Disamban wannan shekara kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

Shadary tsohon ministan harkokin cikin kasar DRC, shi ne babban sakataren jam'iyyar PPRD a halin yanzu.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China