in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD na sa ran Japan za ta gaggauta nemawa wadanda aka bautar ta hanyar lalata hakkokinsu
2018-08-03 10:36:25 cri
Shugaban hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD Zeid Ra'ad Al Hussein, ya yi kira ga gwamnatin kasar Japan, ta gaggauta nemawa wadanda aka bautar ta hanyar lalata yayin yakin duniya na biyu hakkokinsu, domin shekaru na kara cimmusu.

Yayin wani taron manema labarai a hedkwatar MDD dake birnin New York, Zeid Al Hussein, ya ce wadanda aka bautar ta hanyar lalata a Koriya ta kudu da Koriya ta arewa da kasar Sin da sauran kasashe, na kara girma, kuma suna da bukatar sanin ko za a yi raradin da suke ji adalci.

Jami'in wanda ya ce ya kamata a gaggauta daukar mataki, ya ce wannan shi ne kiran da zai yi ga gwamnatin Japan.

Ya kuma bayyana fatan Japan za ta yi komai a bayyane game da yuwuwar sake gyara ka'idojin yarjejeniyar da aka cimma da Koriya ta arewa a shekarar 2015 kan batun, wadda wadanda lamarin ya shafa da gwamnati mai ci suka ki amincewa da ita. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China