in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Antonio Guterres ya yi kira da a kara kwazo wajen dakile safarar bil Adama
2018-07-31 10:40:59 cri
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi kira da a kara kwazo wajen dakile safarar bil Adama. Mr. Guterres ya bayyana hakan ne, albarkacin ranar yaki da safarar bil Adama ta kasa da kasa, yana mai cewa hakan laifi ne da ya shafi dukkanin sassan duniya.

Babban magatakardar MDDr ya kara da cewa, masu safarar bil Adama na aikata wannan laifi ba tare da tausayi ba, kuma da dama daga wadanda ake cutarwa, ba sa samun wata kulawa ta musamman.

Ya ce safarar bil Adama na aukuwa ne sakamakon rashin daidaito tsakanin al'umma, da tashe tashen hankula dake aukuwa a kasashe da yankuna daban daban, lamarin dake tauyewa al'ummu da dama hakkokin su na bil Adama.

Kaza lika yara kanana, da matasa, da 'yan ci rani, da bakin haure, su ne ke sahun gaba wajen fadawa tarkon masu fataucin mutane. Yayin da mata da 'yan mata ke fuskantar kaskanci, sakamakon wannan mummunan laifi. Mr Guterres ya ce ana jefa rayuwar mata da dama cikin ayyukan rashin da'a, da karuwanci, da auren dole ta hanyar fataucin mutane. Yayin da a wasu lokuta ake cire sassan jikin mutanen da suka tsinci kan su a hannun masu fataucin bil Adama.

Daga nan sai Mr. Guterres ya bayyana aniyar MDD, game da yaki da masu fataucin mutane, da tabbatar da ana hukunta dukkanin wadanda aka kama suna aikata hakan, tare da tallafar rayuwar wadanda hakan ya shafa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China